9 Kada kuma mu gwada Ubangiji yadda waɗansu suka yi, har macizai suka hallaka su.
10 Kada kuma mu yi gunaguni yadda waɗansu suka yi, har mai hallakarwa ya hallaka su.
11 To, duk wannan ya same su ne a kan misali, an kuma rubuta shi ne don a gargaɗe mu, mu da ƙarshen zamani ya zo mana.
12 Don haka duk wanda yake tsammani ya kahu, ya mai da hankali kada ya fāɗi.
13 Ba wani gwajin da ya taɓa samunku, wanda ba a saba yi wa ɗan adam ba. Allah mai alkawari ne, ba zai kuwa yarda a gwada ku fin ƙarfinku ba, amma a game da gwajin sai ya ba da mafita, yadda za ku iya jure shi.
14 Saboda haka, ya ƙaunatattuna, ku guji bautar gumaka.
15 Ina magana da ku a kan ku mahankalta ne fa, ku duba da kanku ku ga abin da nake faɗa.