4 cewa an binne shi, an ta da shi a rana ta uku, kamar yadda Littattafai suka faɗa,
5 ya kuma bayyana ga Kefas, sa'an nan ga sha biyun.
6 Sa'an nan ya bayyana ga 'yan'uwa fiye da ɗari biyar a lokaci guda, yawancinsu kuwa suna nan har zuwa yanzu, amma waɗansu sun yi barci.
7 Sa'an nan ya bayyana ga Yakubu, sa'an nan ga dukan manzanni.
8 Daga ƙarshen duka ya bayyana a gare ni, ni ma da nake kasasshe, marar cancanta.
9 Don ni ne mafi ƙanƙanta a cikin manzanni, ban ma isa a ce da ni manzo ba, saboda na tsananta wa Ikkilisiyar Allah.
10 Amma saboda alherin Allah na zama yadda nake, alherin da ya yi mini kuwa ba a banza yake ba. Har ma na fi kowannensu aiki, ba kuwa ni ba, alherin Allah ne da yake zuciyata.