2 sai ga wani mutum da aka haifa gurgu, ana ɗauke da shi. Kowace rana kuwa akan ajiye shi a ƙofar Haikali, wadda ake kira Ƙawatacciyar Ƙofa, don ya roƙi sadaka ga masu shiga Haikali.
3 Da ganin Bitrus da Yahaya suna shiga Haikalin, ya roƙe su sadaka.
4 Bitrus kuwa ya zuba masu ido, tare da Yahaya, ya ce, “Dube mu.”
5 Sai kuwa duk hankalinsa ya koma a kansu, da tsammanin samun wani abu a gunsu.
6 Amma Bitrus ya ce, “Kuɗi kam, ba ni da su, amma abin da nake da shi, shi zan ba ka. Da sunan Yesu Almasihu Banazare, yi tafiya.”
7 Sai Bitrus ya kama hannunsa na dama, ya tashe shi. Nan tāke ƙafafunsa da wuyan sawunsa suka yi ƙarfi.
8 Wuf, sai ya zabura, ya miƙe tsaye, ya fara tafiya, ya shiga Haikalin tare da su, yana tafe, yana tsalle, yana kuma yabon Allah.