1 Wata rana yana koyar da mutane a Haikali, yana yi musu bishara, sai ga manyan firistoci da malaman Attaura, da shugabanni suka matso,
2 suka ce masa, “Gaya mana da wane izini kake yin abubuwan nan, ko kuwa wa ya ba ka izinin?”
3 Sai ya amsa musu ya ce, “Ni ma zan yi muku wata tambaya. Ku gaya mini,
4 baftismar da Yahaya ya yi, daga Sama take, ko kuwa ta mutum ce?”