42 Domin Dawuda da kansa a Zabura ya ce,‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina,“Zauna a damana,
43 Sai na sa ka take maƙiyanka.” ’
44 Dawuda ya ce shi Ubangiji ne. To, ƙaƙa zai zama ɗansa?”
45 Ya ce wa almajiransa a gaban dukan jama'a,
46 “Ku yi hankali da malaman Attaura, masu son yawo a cikin manyan riguna, masu so a gaishe su a kasuwa, masu son mafifitan mazaunai a majami'u, da mazaunan alfarma a wurin biki.
47 Su ne masu cin kayan matan da mazansu suka mutu, masu yin doguwar addu'a don ɓad da sawu. Su za a yi wa hukunci mafi tsanani.”