16 Saboda haka, zan yi masa bulala in sake shi.”[
17 A lokacin idi kuwa lalle ne ya sakar musu ɗaurarre guda.]
18 Amma duk suka ɗauki ihu gaba ɗaya, suna cewa, “A yi da wannan ɗin, a sakar mana Barabbas!”
19 (Barabbas shi ne wani mutum da aka jefa a kurkuku, saboda wani tawayen da aka yi a birni, da kuma kisankai.)
20 Sai Bilatus ya sāke yi musu magana, don yana so ya saki Yesu.
21 Amma suka yi ta ƙwala ihu, suna cewa, “A gicciye shi! A gicciye shi!”
22 Ya sāke faɗa musu, a faɗa ta uku, “Ta wane hali? Wane mugun abu ya yi? Ai, ban sami dalilin kisa a gare shi ba. Saboda haka, zan yi masa bulala in sake shi.”