39 Ku dubi hannuwana da ƙafafuna, ai, ni ne da kaina. Ku taɓa ni, ku ji, don fatalwa ba ta da nama da ƙashi, yadda kuke gani nake da su.”
40 Da ya faɗi haka, ya nuna musu hannuwansa da ƙafafunsa.
41 Amma tun suna da sauran shakka saboda tsananin farin ciki da mamaki, sai ya ce musu, “Kuna da wani abinci a nan?”
42 Sai suka ba shi wata tsokar gasasshen kifi.
43 Ya kuwa karɓa, ya ci a gabansu.
44 Ya kuma ce musu, “Wannan ita ce maganata da na gaya muku tun muna tare, cewa lalle ne a cika duk abin da yake rubuce game da ni a Attaura ta Musa, da littattafan annabawa, da kuma Zabura.”
45 Sa'an nan ya wayar da hankalinsu su fahimci Littattafai,