1 Sai ya tara goma sha biyun nan ya ba su iko da izini kan dukan aljannu, su kuma warkar da cuce-cuce,
2 ya kuma aike su su yi wa'azin Mulkin Allah, su kuma warkar da marasa lafiya.
3 Ya kuma ce musu, “Kada ku ɗauki wani guzuri a tafiyarku, ko sanda, ko burgami, ko gurasa, ko kuɗi. Kada kuma ku ɗauki taguwa biyu.
4 Duk gidan da kuka sauka, ku zauna a nan har ku tashi.