1 Sai Yesu ya tashi daga nan, ya tafi ƙasar Yahudiya, da kuma hayin Kogin Urdun. Taro kuma ya sāke haɗuwa wurinsa, ya kuma sāke koya musu kamar yadda ya saba.
2 Sai waɗansu Farisiyawa suka zo wajensa don su gwada shi, suka tambaye shi suka ce, “Halal ne mutum ya saki mata tasa?”
3 Sai ya amsa musu ya ce, “Me Musa ya umarce ku?”
4 Suka ce, “Musa ya ba da izini a rubuta takardar kisan aure, a kuma saki matar.”