3 Sai ya amsa musu ya ce, “Me Musa ya umarce ku?”
4 Suka ce, “Musa ya ba da izini a rubuta takardar kisan aure, a kuma saki matar.”
5 Yesu ya ce musu, “Don taurinkanku ne Musa ya rubuta muku wannan umarni.
6 Amma tun farkon halitta ‘Allah ya halicce su, namiji da tamata.’
7 ‘Don haka fa sai mutum yă bar uwa tasa da ubansa, yă manne wa mata tasa.
8 Haka su biyun nan su zama jiki guda.’ Har nan gaba su zama ba jiki biyu ba ne, ɗaya ne.
9 Abin da Allah fa ya gama, kada mutum ya raba.”