5 Yesu ya ce musu, “Don taurinkanku ne Musa ya rubuta muku wannan umarni.
6 Amma tun farkon halitta ‘Allah ya halicce su, namiji da tamata.’
7 ‘Don haka fa sai mutum yă bar uwa tasa da ubansa, yă manne wa mata tasa.
8 Haka su biyun nan su zama jiki guda.’ Har nan gaba su zama ba jiki biyu ba ne, ɗaya ne.
9 Abin da Allah fa ya gama, kada mutum ya raba.”
10 A cikin gida kuma sai almajiransa suka sāke tambayarsa wannan magana.
11 Sai ya ce musu, “Kowa ya saki mata tasa, ya auri wata, zina yake yi da ta biyun.