47 Amma ɗaya daga cikin na tsaye, ya zaro takobinsa, ya kai wa bawan babban firist sara, ya dauke masa kunne.
48 Sai Yesu ya ce musu, “Kun fito ne da takuba da kulake ku kama ni kamar ɗan fashi?
49 Kowace rana ina tare da ku a Haikalin ina koyarwa, amma ba ku kama ni ba. Amma an yi haka ne fa domin a cika Littattafai.”
50 Daga nan duk almajiran suka yashe shi, suka yi ta kansu.
51 Sai wani saurayi, daga shi sai mayafi, ya bi shi. Suka kai masa cafka,
52 shi kuwa ya bar musu mayafin, ya gudu huntu.
53 Daga nan suka tafi da Yesu wurin babban firist. Duk manyan firistoci da shugabanni da malaman Attaura suka taru a wurinsa.