1 Da Asabar ta wuce, Maryamu Magadaliya, da Maryamu uwar Yakubu, da kuma Salome, suka sayo kayan ƙanshi, domin su je su shafa masa.
2 A ranar farko ta mako, da assussuba suka tafi kabarin, da fitowar rana sai suka isa.
3 Suna ce wa juna, “Wa zai mirgine mana dutsen nan daga bakin kabarin?”
4 Da suka ɗaga kai, suka ga, ashe, an mirgine dutsen waje ɗaya, ga shi kuwa, ƙato ne ƙwarai.
5 Suna shiga kabarin, sai suka ga wani saurayi a zaune daga dama, saye da farar riga. Sai suka firgita.