1 Suka iso hayin teku a ƙasar Garasinawa.
2 Da saukarsa daga jirgin, sai ga wani mai baƙin aljan daga makabarta ya tarye shi.
3 Shi kuwa makabarta ce mazauninsa. Ba mai iya ɗaure shi kuma, ko da sarƙa ma.
4 Don dā an sha ɗaure shi da mari da sarƙa, amma ya tsintsinka sarƙar, ya gutsuntsuna marin, har ma ba mai iya bi da shi.
5 Kullum kuwa dare da rana yana cikin makabarta, da kan duwatsu, yana ta ihu, yana kukkuje jikinsa da duwatsu.
6 Da dai ya hango Yesu, sai ya sheƙo a guje ya fāɗi a gabansa,