25 Sai ga wata mace wadda ta shekara goma sha biyu tana zub da jini,
26 ta kuma sha wahala da gaske a hannun masu magani da yawa, har ta ɓad da duk abin da take da shi, amma duk a banza, sai ma gaba-gaba cutar take yi.
27 Da ta ji labarin Yesu, ta raɓo ta bayansa cikin taron, ta taɓa mayafinsa.
28 Don tā ce a ranta, “Ko da tufarsa ma na taɓa, sai in warke.”
29 Nan take zubar jininta ta tsaya, ta kuma ji a jikinta an warkar da cutarta.
30 Nan da nan kuwa da Yesu ya ji wani iko ya fita daga gare shi, sai ya waiwaya a cikin taron, ya ce, “Wa ya taɓa tufata?”
31 Sai almajiransa suka ce masa, “Kana ganin taro na matsarka, ka ce, wa ya taɓa ka?”