1 A lokacin nan da wani taro mai yawan gaske ya sāke haɗuwa, ba su kuwa da abinci, sai ya kira almajiransa, ya ce musu,
2 “Ina jin tausayin wannan taro, don yau kwanansu uku ke nan a guna, ba su da wani abinci.
3 In kuwa na sallame su su tafi gida da yunwa haka, ai, za su kasa a hanya, ga shi kuwa, waɗansunsu sun fito nesa.”
4 Sai almajiransa suka amsa masa suka ce, “Ina za a iya samun gurasar da za ta ciyar da mutanen nan a jeji haka?”
5 Sai ya tambaye su, “Gurasa nawa gare ku?” Suka ce, “Bakwai.”