14 Lalle a kansu ne aka cika annabcin Ishaya cewa,‘Za ku ji kam, amma ba za ku fahimta ba faufau,Za ku kuma gani, amma ba za ku gane ba faufau,
15 Don zuciyar jama'ar nan ta yi kanta,Sun toshe kunnuwansu,Sun kuma runtse idanunsu,Don kada su gani da idanunsu,Su kuma ji da kunnuwansu,Su kuma fahimta a zuciyarsu,Har su juyo gare ni in warkar da su.’
16 Albarka tā tabbata ga idanunku domin suna gani, da kuma kunnuwanku domin suna ji.
17 Hakika, ina gaya muku, annabawa da adalai da yawa sun yi ɗokin ganin abin da kuke gani, amma ba su gani ba, su kuma ji abin da kuke ji, amma ba su ji ba.
18 “To, ga ma'anar misalin mai shukar nan.
19 Wanda duk ya ji Maganar Mulki bai kuma fahimce ta ba, sai Mugun ya zo ya zăre abin da aka shuka a zuciyarsa. Wannan shi ne irin da ya faɗa a hanya.
20 Wanda ya faɗa a wuri mai duwatsu kuwa, shi ne wanda da zarar ya ji Maganar Allah, sai ya karɓa da farin ciki.