15 Da maraice ya yi, almajiransa suka zo gare shi, suka ce, “Wurin nan fa ba kowa, ga shi kuwa, rana ta sunkuya. Sai ka sallami taron, su tafi ƙauyuka su saya wa kansu abinci.”
16 Yesu ya ce, “Ba lalle su tafi ba. Ku ku ba su abinci mana.”
17 Sai suka ce masa, “Ai, gurasa biyar da kifi biyu kawai muke da su a nan.”
18 Sai ya ce, “Ku kawo mini su.”
19 Sa'an nan ya umarci taron su zazzauna a ɗanyar ciyawa. Da ya ɗauki gurasa biyar ɗin da kifi biyun, sai ya ɗaga kai sama, ya yi wa Allah godiya, ya gutsuttsura gurasar, ya yi ta ba almajiransa, almajiran kuma suna bai wa jama'a.
20 Duka kuwa suka ci suka ƙoshi, har suka kwashe ragowar gutsattsarin, cike da kwando goma sha biyu.
21 Waɗanda suka ci kuwa misalin maza dubu biyar ne banda mata da yara.