4 Don dā ma Yahaya ya ce masa bai halatta ya zauna da ita ba.
5 Ko da yake yana son kashe shi, yana jin tsoron jama'a, don sun ɗauka shi annabi ne.
6 To, da ranar haihuwar Hirudus ta kewayo, sai 'yar Hirudiya ta yi rawa a gaban taron, har ta gamshi Hirudus,
7 har ma ya yi mata rantsuwa zai ba ta duk abin da ta roƙa.
8 Amma da uwa tasa ta zuga ta, sai ta ce, “A ba ni kan Yahaya Maibaftisma a cikin akushi yanzu yanzu.”
9 Sai sarki ya yi baƙin ciki, amma saboda rantsuwa tasa da kuma baƙinsa, ya yi umarni a ba ta.
10 Ya aika aka fille wa Yahaya kai a kurkuku,