14 Gama da yawa ake kira, amma kaɗan ne zaɓaɓɓu.”
15 Sai Farisiyawa suka je suka yi shawara yadda za su burma shi cikin maganarsa.
16 Suka aiko almajiransu wurinsa tare da waɗansu mutanen Hirudus, suka ce, “Malam, ai, mun sani kai mai gaskiya ne, sai koyar da tafarkin Allah sosai kake yi, ba ka kuma zaɓen kowa, don ka ɗauki kowa da kowa daidai.
17 To, faɗa mana abin da ka gani. Shin, daidai ne mu biya Kaisar haraji, ko kuwa?”
18 Yesu kuwa domin ya gane muguntarsu, sai ya ce musu, “Don me kuke jarraba ni? Ku munafukai!
19 Ku nuna mini kuɗin harajin.” Sai suka kawo masa dinari.
20 Yesu ya ce musu, “Surar nan da sunan nan na wane ne?”