27 Bayansu duka sai matar ta rasu.
28 To, a tashin matattu, matar wa za ta zama a cikinsu, su bakwai ɗin? Don duk sun aure ta.”
29 Amma Yesu ya amsa musu ya ce, “Kun ɓăta ne, domin ba ku san Littattafai ba, ba ku kuma san ikon Allah ba.
30 Domin a tashin matattu, ba a aure, ba a aurarwa, sai dai kamar mala'ikun da suke Sama ake.
31 Game da tashin matattu, ashe, ba ku taɓa karanta abin da Allah ya ce muku ba? cewa,
32 ‘Ni ne Allahn Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu.’ Ai, waɗanda Allah shi ne Allahnsu rayayyu ne, ba matattu ba.”
33 Da jama'a suka ji haka, sai suka yi mamakin koyarwarsa.