43 Amma dai ku sani, da maigida zai san ko a wane lokaci ne da dare ɓarawo zai zo, da ya zauna a faɗake ya hana a shigar masa gida.
44 Don haka ku ma sai ku zauna a kan shiri, domin a lokacin da ba ku zata ba, Ɗan Mutum zai zo.”
45 “Wane ne amintaccen bawan nan mai hikima, da ubangidansa ya ba shi riƙon gidansa, yă riƙa ba su abincinsu a kan kari?
46 Albarka tā tabbata ga bawan da in ubangidansa ya dawo zai samu yana yin haka.
47 Hakika, ina gaya muku, sai ya ɗora shi a kan dukan mallakarsa.
48 Amma in bawan nan mugu ne, ya kuma ce a ransa, ‘Ubangidana ya jinkirta zuwansa,’
49 sa'an nan ya soma dūkan abokan bautarsa, yana ci yana sha tare da mashaya,