11 Kullum kuna tare da talakawa, amma ba kullum ne kuke tare da ni ba.
12 Zuba man nan da ta yi a jikina, ta yi shi ne domin tanadin jana'izata.
13 Hakika, ina gaya muku, duk inda za a yi bisharar nan a duniya duka, abin da matar nan ta yi za a riƙa faɗarsa don tunawa da ita.”
14 Sai ɗaya daga cikin sha biyun nan, mai suna Yahuza Iskariyoti, ya je wurin manyan firistoci,
15 ya ce, “Me za ku ba ni, in na bashe shi a gare ku?” Sai suka ƙirga kuɗi azurfa talatin, suka ba shi.
16 Tun daga lokacin nan ne ya riƙa neman hanyar da zai bashe shi.
17 To, a ranar farko ta idin abinci marar yisti sai almajiran suka zo wurin Yesu suka ce, “Ina kake so mu shirya maka cin Idin Ƙetarewa?”