66 Me kuka gani?” Suka amsa suka ce, “Ya cancanci kisa!”
67 Sai suka tattofa masa yau a fuska, suka bubbuge shi, waɗansu kuma suka mammare shi,
68 suna cewa, “Yi mana annabci, kai Almasihu! Faɗi wanda ya buge ka!”
69 To, Bitrus kuwa yana zaune a tsakar gida a waje, sai wata baranya ta zo ta tsaya a kansa, ta ce, “Kai ma, ai, tare kake da Yesu Bagalile!”
70 Amma ya musa a gabansu duka ya ce, “Ni ban san abin da kike nufi ba.”
71 Da ya fito zaure, sai wata baranya kuma ta gan shi, ta ce wa waɗanda suke tsaitsaye a wurin, “Ai, mutumin nan tare yake da Yesu Banazare!”
72 Sai ya sāke musawa har da rantsuwa ya ce, “Ban ma san mutumin nan ba.”