26 Kowa ya ji maganar nan tawa, bai aikata ta kuma ba, za a misalta shi da wawan mutum, wanda ya gina gidansa a kan rairayi.
27 Da ruwa ya sauko, koguna suka yi cikowa, sai iska ta taso ta bugi gidan har ya rushe, mummunar ragargajewa kuwa!”
28 Da Yesu ya gama duk wannan magana, sai taro suka yi mamakin koyarwarsa,
29 domin yana koya musu da hakikancewa, ba kamar malamansu na Attaura ba.