1 Tun fil'azal akwai Kalma, Kalman nan kuwa tare da Allah yake, Kalman nan kuwa Allah ne.
2 Shi ne tun fil'azal yake tare da Allah.
3 Dukan abubuwa sun kasance ta gare shi ne, ba kuma abin da ya kasance na abubuwan da suka kasance, sai ta game da shi.
4 Shi ne tushen rai, wannan rai kuwa shi ne hasken mutane.
5 Haske na haskakawa cikin duhu, duhun kuwa bai rinjaye shi ba.
6 Akwai wani mutum da Allah ya aiko, mai suna Yahaya.
7 Shi fa ya zo shaida ne, domin ya shaidi hasken, kowa yă ba da gaskiya ta hanyarsa.