3 Dukan abubuwa sun kasance ta gare shi ne, ba kuma abin da ya kasance na abubuwan da suka kasance, sai ta game da shi.
4 Shi ne tushen rai, wannan rai kuwa shi ne hasken mutane.
5 Haske na haskakawa cikin duhu, duhun kuwa bai rinjaye shi ba.
6 Akwai wani mutum da Allah ya aiko, mai suna Yahaya.
7 Shi fa ya zo shaida ne, domin ya shaidi hasken, kowa yă ba da gaskiya ta hanyarsa.
8 Ba shi ne hasken ba, ya zo ne domin ya shaidi hasken.
9 Akwai hakikanin haske mai shigowa duniya da yake haskaka kowane mutum.