26 Amma ku ba ku gaskata ba, domin ba kwa cikin tumakina.
27 Tumakin nan nawa sukan saurari muryata, na san su, suna kuma bi na.
28 Ina ba su rai madawwami, ba kuwa za su halaka ba har abada, ba kuma mai ƙwace su daga hannuna.
29 Ubana, wanda ya ba ni su, ya fi duka girma, ba kuwa mai iya ƙwace su daga ikon Uban.
30 Ni da Uba ɗaya muke.”
31 Sai Yahudawa suka sāke ɗebo duwatsu su jajjefe shi.
32 Yesu ya amsa musu ya ce, “Na nuna muku ayyuka nagari masu yawa daga wurin Uba, a kan wanne a cikinsu za ku jajjefe ni?”