18 Betanya kuwa kusa da Urushalima take, misalin mil biyu.
19 Yahudawa da yawa sun zo su yi wa Marta da Maryamu ta'aziyyar ɗan'uwansu.
20 Da jin Yesu na zuwa, sai Marta ta je taryensa, Maryamu kuwa ta zauna a gida.
21 Sai Marta ta ce wa Yesu, “Ya Ubangiji, da kana nan da ɗan'uwana bai mutu ba.
22 Ko yanzu ma na sani kome ka roƙi Allah zai yi maka.”
23 Yesu ya ce mata, “Ɗan'uwanki zai tashi.”
24 Marta ta ce masa, “Na sani zai tashi a tashin matattu a ranar ƙarshe.”