38 domin a cika faɗar Annabi Ishaya cewa,“Ya Ubangiji, wa ya gaskata jawabinmu?Ga wa kuma aka bayyana ikon Ubangiji?”
39 Shi ya sa ba su iya ba da gaskiya ba. Domin Ishaya ya sāke cewa,
40 “Ya makantar da su, ya kuma taurarar da zuciya tasu,Kada su gani da idanunsu, su kuma gane a zuci,Har su juyo gare ni in warkar da su.”
41 Ishaya ya faɗi haka saboda ya ga ɗaukakar Almasihu, ya kuma ba da labarinsa.
42 Duk da haka, da yawa har daga cikin shugabanni ma suka gaskata da shi, amma saboda tsoron Farisiyawa, ba su bayyana ba, don kada a fisshe su daga jama'a.
43 Don sun fi ƙaunar girmamawar mutane da girmamawar Allah.
44 Sai Yesu ya ɗaga murya ya ce, “Wanda yake gaskatawa da ni, ba da ni yake gaskatawa ba, amma ga wanda ya aiko ni ne.