11 Don ya san wanda zai bāshe shi, shi ya sa ya ce, “Ba dukanku ne tsarkakakku ba.”
12 Bayan ya wanke ƙafafunsu, ya yafa mayafinsa, sai ya sāke kishingiɗa, ya ce musu, “Kun gane abin da na yi muku?
13 Kuna kirana Malam, da kuma Ubangiji. Daidai ne kuwa, don haka nake.
14 Tun da yake ni Ubangijinku da kuma Malaminku, har na wanke muku ƙafa, ashe, ku ma wajibi ne ku wanke wa juna.
15 Na yi muku ishara domin ku ma ku yi yadda na yi muku
16 Lalle hakika, ina gaya muku, bawa ba ya fin ubangijinsa, manzo kuma ba ya fin wanda ya aiko shi.
17 In dai kun san wannan, kuna kuma aikatawa, ku masu farin ciki ne.