1 To, da Ubangiji Yesu ya sani dai Farisiyawa sun ji labari yana samun almajirai, yana kuma yi musu baftisma fiye da Yahaya
2 (ko da yake dai ba Yesu kansa yake yin baftisma ba, almajiransa ne),
3 sai ya bar ƙasar Yahudiya, ya koma ƙasar Galili.
4 Lalle ne kuwa yă ratsa ƙasar Samariya.
5 Sai ya zo wani gari na ƙasar Samariya, wanda ake kira Saikar, kusa da yankin ƙasar da Yakubu ya ba ɗansa Yusufu.
6 Rijiyar Yakubu kuwa a nan take. Saboda gajiyar tafiya fa, sai Yesu ya zauna haka nan a bakin rijiyar. Wajen tsakar rana ce kuwa.