28 Sai matar ta bar tulunta, ta koma gari, ta ce wa mutane,
29 “Ku zo, ku ga mutumin da ya gaya mini duk abin da na taɓa yi! Shin, ko wannan shi ne Almasihu?”
30 Sai suka fito daga garin suka nufo shi.
31 Ana cikin haka sai almajiran suka roƙe shi suka ce, “Ya shugaba, ci abinci.”
32 Amma ya ce musu, “Ina da abincin da ba ku sani ba.”
33 Almajiran suka ce wa juna, “Shin, wani ya kawo masa abinci ne?”
34 Sai Yesu ya ce musu, “Abincina shi ne in aikata nufin wanda ya aiko ni, in kuma cika aikinsa.