26 Yadda Uba kansa yake tushen rai, haka ya sa Ɗan ya zama tushen rai.
27 Ya kuma ba shi ikon zartar da hukunci, saboda shi Ɗan Mutum ne.
28 Kada ku yi mamakin wannan, domin lokaci na zuwa da duk waɗanda suke kaburbura za su ji murya tasa,
29 su kuma fito, waɗanda suka aikata nagarta su tashi, tashin rai, waɗanda suka yi rashin gaskiya kuwa su tashi, tashin hukunci.
30 “Ba na iya yin kome ni kaɗai. Yadda nake ji, haka nake yin hukunci. Hukuncina kuwa na adalci ne, domin ba nufin kaina nake bi ba, sai dai nufin wanda ya aiko ni.
31 In na shaida kaina, shaidata ba tabbatacciya ba ce.
32 Akwai wani mashaidina dabam, na kuwa san shaidar da yake yi mini tabbatacciya ce.