46 Sai dogaran suka amsa suka ce, “A'a, ba mutumin da ya taɓa magana kamar wannan!”
47 Sai Farisiyawa suka amsa musu suka ce, “Af! Har ku ma an ɓad da ku ne?
48 Ashe, akwai wani daga cikin shugabanni ko Farisiyawa da ya gaskata da shi?
49 Amma wannan taro da ba su san Attaura ba, ai, la'anannu ne.”
50 Nikodimu kuwa da ya je wurinsa dā, yana kuwa ɗaya daga cikinsu, ya ce musu,
51 “Ashe, shari'armu takan hukunta mutum tun ba a ji daga bakinsa ba, an kuma san abin da yake ciki?”
52 Suka amsa masa suka ce, “Kai ma Bagalile ne? Bincika mana ka gani, ai, ba wani annabi da zai bayyana a ƙasar Galili.”[