8 Ku dai ku tafi idin. Ni ba za ni ba yanzu, don lokacina bai yi sosai ba tukuna.”
9 Da ya faɗa musu haka, ya dakata a ƙasar Galili.
10 Bayan 'yan'uwansa sun tafi idin kuwa, shi ma ya tafi, amma a ɓoye, ba a fili ba.
11 Yahudawa suna ta nemansa a wurin idin suna cewa, “Ina yake ne?”
12 Taro kuma suka riƙa maganarsa a raɗe, waɗansu na cewa, “Mutum ne nagari.” Waɗansu kuma na cewa, “A'a, ai, ɓad da jama'a yake.”
13 Amma ba wanda ya yi magana tasa a fili don tsoron Yahudawa.
14 Wajen tsakiyar idin sai Yesu ya shiga Haikali ya koyar.