1 Yesu kuwa ya hau Dutsen Zaitun.
2 Da sassafe kuma ya sāke shiga Haikali. Duk mutane suka zo wurinsa, ya kuwa zauna yana koya musu.
3 Sai malaman Attaura da Farisiyawa suka kawo wata mace da aka kama da zina. Da suka tsai da ita a tsaka,
4 suka ce masa, “Malam, matan nan an kama ta ne, suna cikin yin zina.