32 Tun da aka fara duniya ba a taɓa jin wani ya buɗe idon wanda aka haifa makaho ba.
33 Da mutumin nan ba daga Allah ya fito ba, da ba abin da zai iya yi.”
34 Suka amsa masa suka ce, “Kai da aka haifa a baƙin zunubi ne za ka koya mana?” Sai suka kore shi.
35 Yesu ya ji labari sun kore shi. Da ya same shi, ya ce, “Ka gaskata da Ɗan Mutum ko?”
36 Ya amsa ya ce, “Wane ne shi, ya Shugaba, da zan gaskata da shi?”
37 Yesu ya ce masa, “Ai, ka gan shi, shi ne ma mai magana da kai.”
38 Sai ya ce, “Ya Ubangiji, na ba da gaskiya,” ya kuma yi masa sujada.