39 Zan wahalar da zuriyar Dawuda, amma ba har abada ba.’ ”
40 Sulemanu kuwa ya nema ya kashe Yerobowam, amma Yerobowam ya tashi, ya tsere zuwa Masar, wurin Shishak Sarkin Masar, ya zauna a can har rasuwar Sulemanu.
41 Sauran ayyukan Sulemanu, da dukan abin da ya yi, da hikimarsa an rubuta su a littafin tarihin Sulemanu.
42 Sulemanu ya yi shekara arba'in yana sarauta a Urushalima a kan Isra'ila duka.
43 Sulemanu ya rasu, aka binne shi a birnin Dawuda, wato Urushalima. ‘Dansa Rehobowam ya gaji sarautarsa.