1 “Na gaji da rayuwa,Ku ji ina fama da baƙin ciki.
2 Kada ka hukunta ni, ya Allah.Ka faɗa mini laifin da kake tuhumata da shi.
3 Daidai ne a gare ka ka yi mugunta?Ka wulakanta abin da kai da kanka ka yi?Sa'an nan ka yi murmushi saboda dabarun mugaye?
4 Yadda mutane suke duban abu, haka kake duba?
5 Kai ma ranka gajere ne kamar namu?
6 In haka ne, me ya sa kake bin diddigin dukan laifofina,Kana farautar dukan abin da na yi?
7 Ka sani, ba ni da laifi,Ka kuma sani, ba wanda zai cece ni daga gare ka.