1 Ayuba ya yi magana.
2 “Ai, na taɓa jin magana irin wannan,Ta'aziyyar da kake yi azaba ce kawai.
3 Ka dinga yin magana ke nan har abada?A kullum maganarka ita ce dahir?
4 In da a ce a matsayina kake, ni kuma ina a naka,Ina iya faɗar duk abin da kake faɗa yanzu.Da sai in kaɗa kaina da hikima,In dulmuyar da kai a cikin rigyawar maganganu.
5 Da sai in ba ka shawara ta ƙarfafawa,In yi ta yi maka maganar ta'azantarwa.
6 “Amma ba abin da zan faɗa wanda zai taimaka,Yin shiru kuma ba zai raba ni da azaba ba.
7 Ka gajiyar da ni, ya Allah,Ka shafe iyalina.