9 Tarko ya kama diddigensa ya riƙe shi,
10 An binne masa tarko a ƙasa,An kafa masa tarko a hanyarsa.
11 “Kewaye da shi duka razana tana jiransa,Duk inda ya nufa tana biye da shi,
12 Dā attajiri ne, amma yanzu ya talauce,Kusa da shi bala'i na tsaye yana jiransa.
13 Mummunan ciwo ya bazu ko'ina a jikinsa,Yana sa hannuwansa da ƙafafunsa su ruɓe,
14 Dā yana zaune lafiya,Sai razana ta tatike shi,Ta jawo shi zuwa ga Sarkin Mutuwa.
15 Yanzu kowa zai iya zama a alfarwarsa,Bayan da an karkashe ƙwayoyin cuta da farar wuta.