18 'Yan yara sukan raina ni su yi mini dariya sa'ad da suka gan ni.
19 Aminaina na kusa sukan dube ni, duban ƙyama,Waɗanda na fi ƙaunarsu duka sun zama maƙiyana.
20 Fatar jikina ta saki, ba ƙarfi,Da ƙyar na kuɓuta.
21 Ku abokaina ne! Ku ji tausayina!Ikon Allah ya fyaɗa ni ƙasa.
22 Me ya sa kuke ɓata mini rai kamar yadda Allah ya yi?Azabar da kuka yi mini har yanzu ba ta isa ba?
23 “Da ma a ce wani zai rubuta abin da nake faɗa,Ya rubuta shi a littafi!
24 Ko kuwa ya zana kalmomina da kurfi a kan dutse,Ya rubuta su don su tabbata har abada!