17 Zai mutu bai ga kogunan man zaitun ba,Ba kuwa zai ga rafuffukan da suke da yalwar albarka ba.
18 Tilas ya rabu da dukan abin da ya yi wahalarsa.Ba dama ya mori dukiyarsa,
19 Saboda zalunci da rashin kula da matalauta,Da ƙwace gidajen da waɗansu suka gina.
20 “Har abada ba zai kai ga samun abin da yake wahala ba.
21 Sa'ad da ya ci ba zai yi saura ba,Gama yanzu dukiyarsa ta ƙare.
22 A lokacin da yake gaɓar samunsa,Baƙin ciki mai nauyin gaske zai ragargaza shi.
23 Bari ya ci duk irin abin da yake so!Allah zai hukunta shi da hasala da fushi.