15 Suna tsammani ba amfani a bauta wa Allah,Ko a yi addu'a gare shi domin samun wata fa'ida.
16 Sukan ce ta wurin ƙarfinsu ne suka yi nasara,Amma ban yarda da irin tunaninsu ba.
17 “An taɓa kashe hasken mugun mutum?Ko masifa ta taɓa fāɗa wa wani daga cikinsu?Allah ya taɓa hukunta wa mugu da fushi,
18 Ya kuma sa su zama kamar tattakar da iska yake kwashewa?Ko kuma kamar ƙura wadda hadiri yake kwashewa?
19 “Kukan ce Allah yakan hukunta yaro saboda zunuban mahaifinsa.A'a! Allah dai yakan hukunta wa masu zunubi.Ya kuma nuna ya yi haka saboda zunubansu ne.
20 Bari dai a hukunta masu zunubiSu kuma ga hasalar Allah.
21 Bayan rasuwar mutum,Ruwansa ne ya sani ko 'ya'yansa suna jin daɗi?