27 “Na san irin tunaninku na hassada,
28 Kuna ta tambaya, ‘Ina ne gidan babban mutumin nan yanzu,Wato mutumin da yake aikata mugunta?’
29 “Ashe, ba ku yi magana da matafiya ba?Ba ku kuma san rahoton da suka kawo ba?
30 A ranar da Allah ya yi fushi, ya yi hukunci,A kullum mugun ne kaɗai yakan kuɓuta.
31 Ba wanda zai fito fili ya zargi mugun,Ko ya mayar masa da martani.
32 Sa'ad da aka ɗauke shi zuwa hurumi,A inda ake tsaron kabarinsa,
33 Dubban mutane sukan tafi wurin jana'izarsa,Akan mai da ƙasa a kan gawarsa a hankali.