3 Gaskiyar da kake yi za ta amfani Allah?Ko kuwa abin kirki da kake yi zai taimake shi?
4 Ai, ba don tsoron Allah da kake yi ba ne,Ya sa wannan tsautawa da jarrabawa suka same ka.
5 Ko kusa ba haka ba ne,Amma saboda zunubi mai yawa da ka yi ne.Saboda kuma dukan muguntar da ka aikata.
6 Don ka sa ɗan'uwanka ya biya ka bashin da kake binsa,Ka ƙwace tufafinsa, ka bar shi huntu.
7 Ka hana wa waɗanda suke ji ƙishi ruwan sha,Ka hana waɗanda suke jin yunwa abinci.
8 Ka mori ikonka da matsayinka,Don ka mallaki dukan ƙasar.
9 Ba ƙin taimako kaɗai ka yi ba,Amma har marayu ma ka yi musu ƙwace, ka wulakanta su.