20 Ba wanda zai tuna da shi,mahaifiyarsa ma ba za ta lura da shi ba.Tsutotsi sukan ci shi su hallaka shi sarai.Za a sare mugunta kamar itace.
21 Haka yake samun wanda ya wulakanta gwauraye.Bai kuma nuna alheri ga matan da ba su haihu ba.
22 Allah, da ikonsa, yakan hallaka masu ƙarfi,Allah yakan aikata, sai mugun mutum ya mutu.
23 Ya yiwu Allah ya bar shi ya yi zamansa lafiya,Amma a kowane lokaci zai sa ido a kansa.
24 Mugun mutum yakan ci nasara ɗan lokaci,Daga nan sai ya yi yaushi kamar tsiro,Ya yi yaushi kamar karan dawa da aka yanke.
25 Akwai wanda zai iya cewa, ba haka ba ne?Akwai wanda zai tabbatar da cewa kalmomina ba gaskiya ba ne?”