7 “Bari maƙiyina ya zama kamar mugun mutum,Wanda ya tashi gāba da ni ya zama kamar marar adalci.
8 Wace sa zuciya take ga marar tsoron Allah?Sa'ad da Allah ya datse shi, ya ɗauke ransa?
9 Allah kuwa zai ji kukansa sa'ad da wahala ta same shi?
10 Ko Mai Iko Dukka zai zama abin farin ciki a gare shi?Ko zai yi kira ga Allah a kowane lokaci?
11 “Zan koya muku zancen ikon Allah,Abin da yake na wajen Mai Iko Dukka ba zan ɓoye ba.
12 Ga shi kuwa, dukanku kun gani da kanku,Me ya sa kuka zama wawaye?
13 “Wannan shi ne rabon mugaye daga wurin Allah,Gādo ne kuma wanda azzalumai za su karɓa daga wurin Mai Iko Dukka.