20 “To, daga ina hikima ta fito?A wane wuri kuma haziƙanci yake?
21 Ba talikin da ya iya ganinta,Ko tsuntsun da yake tashi sama.
22 Halaka da Mutuwa sun ce,‘Da kunnuwanmu mun ji ƙishin-ƙishin a kanta.’
23 “Allah ne kaɗai ya san hanya zuwa gare ta,Ya san inda hikima take,
24 Saboda yana ganin duniya ɗungum,Yana ganin duk abin da yake ƙarƙashin sararin sama.
25 Sa'ad da Allah ya sa iska ta hura,Ya yi wa tekuna iyaka.
26 Sa'ad da ya ba da umarni ga ruwan sama,Da kuma hanyar da tsawa za ta bi,